Sai dai daga baya Muka gano ashe a afirka ta kudu abun ya faru
Mutanen yankin KwaZulu na cike da fargaba bayan da aka gano gawar Zanele Hlatshwayo mai shekara 25, an ciccire wasu sassan jikinta, a kuayen Shayamoya a Afirka Ta Kudu.
Iyayen yarinyar wacce ta bata tun a watan Yuli, sun yi amannar cewa tana daga cikin wadanda masu cin naman mutane ne suka kashe, inda tuni aka kama biyar daga cikinsu.
Da farko dai 'yan sanda sun ki saurarar batun mutumin da ya mika musu kan nasa, amma sai suka yarda da abin da yake fada a lokacin da suka ga jini dumu-dumu a hannayensa da kafafuwansa, suka kuma kama shi.
N
Mutumin ya kai 'yan sandan gidansa, inda aka samu kunnen mutum har takwas a cikin tukunya.
An yi amannar cewa ya yi niyyar sayarwa abokan huldarsa ne, wadanda aka shaida wa cewar suna da sirri na taimakawa mutum ya yi kudi ko ya samu mulki.
An kuma samu wasu sassan jikin da dama a wani akwati.

Post a Comment